1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kasashen duniya na kokarin sassanta rikicin Venezuela

Yusuf Bala Nayaya AH
February 8, 2019

Kungiyar tarayyar Turai da wasu kasashe 13 na yankin Latin Amirka sun cimma matsaya da ke zama ta lalama wajen warware rikicin siyasa da ya dabaibaye kasar Venezuela.

https://p.dw.com/p/3D0yT
Uruguay Montevideo | Treffen Kontaktgruppe zur Staatskrise in Venezuela | Rodolfo Nin Novoa & Federica Mogherini
Rodolfo Nin Novo ministan harkokin waje na Yurugai tare da sakatariyar harkokin waje ta kungiyar tarrayar Turai Federica Mogherini a birnin Montevideo na Yurugai a taron tattauna rikicin siyasar VenezuelaHoto: Getty Images/AFP/P. Porciuncula

A ranar Alhamis ne dai aka yi taron da ke zama na tuntuba tsakanin kasa wanda kuma ya samu goyon bayan kungiyar tarayyar Turai. Jakadu na kasashen Latin Amirka 13 da wakilan kungiyar EU sun halarci taron. Bayan kwashe sa'oi hudu ana muhawara ba tare da sa ido na 'yan jarida ba shugabar sashin kula da harkokin kasashen waje na EU Federica Mogherini da Shugaban kasar Yurugai Tabare Vazquez sun yi taron manema labarai inda suka ce zaman tattaunawar da suka yi,  ya yi amfani kasancewar sun cimma matsaya ta ganin an warware rikicin siyasar Venezuela cikin lumana. Haka zalika a cewar Mogherini, za su kuma ba da tallafi: Ta ce: ''har ila yau tattaunawar da aka yi ta nunar da cewa an fahimci miliyoyin al'umma na cikin hali na kaka na ka yi  don haka kasashen sun amince da hada hannu wuri guda a ba da tallafi. Za a kuma a yi aikin tallafi bisa jagoraci na hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD karkashin jagoranci na  Edwardo Stein."