1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Neman dorewar dimokradiyya a Tunisiya

Mahmud Yaya Azare/ASDecember 23, 2014

Sabon shugaban Tunisiya Caid Beji Essebsi da wanda ya kayar a zaben da aka yi a karshen mako sun bukaci magoya bayansu da su hada don ciyar da dimokradiyya gaba.

https://p.dw.com/p/1E99s
Tunesien/ Präsidentenwahl/ Beji Caid Essebsi
Hoto: Reuters

Shugaba Beji Caid Elsibsi da Moncef Marzouki da aka kayar zaben shugaban kasar sun bukaci hadin kan magoya byansu da al'ummar kasar ce da nufin ganin sun hade waje guda don ciyar kasar gaba. Wannan kira na shugabannin biyu ya zo ne bayan da a hukumance aka bayyana Mr. Essebsi a matsayin wanda ya samu nasara a zagaye na biyu na zaben.

Bangarorin biyu dai suka ce wannan kira ya zama wajibi don ganin kasar ta samu cigaba mai mai'ana da duma samun sukunin dorewar mulkin dimokradiyya wanda ke cikin jerin abubuwan da suka sanya aka yi juyin juya halin da ya kifar da gwamnatin Zainul Abideen Bn Ali a shekarun da suka gabata.

Kombi-Bild Beji Caid Essebsi und Moncef Marzouki
Beji Caid Essebsi da Moncef Marzouki na son dorewar dimokradiyya a Tunisiya

Da ya ke jawabi ga al'ummar kasar shugaban kasar mai barin gado kana wanda ya sha kaye a zaben na ranar Lahadi Moncef Marzouki cewa ya yi "wannan shi ne tafarkin dimokiradiyya na farko da muka fara gogayya da shi a kasarmu, don haka bai kamata mu bata rawarmu da tsalle ba ta hanyar kin amincewa da sakamakon da akwatunan zabe suka nuna. Ina kira ga magoya bayana da yan kasa da kowa ya kai zuciya nesa kana a bawa sabon shugaba cikakken hadin kai"

Präsidentenwahlen in Tunesien
Al'ummar Tunisiya na maraba da samun gwamnatin da ke kan doron dimokradiyyaHoto: picture-alliance/dpa

Shi kuwa sabon shugaban mai jiran gado Beji Caid Essebsibayan godiya ga abokin takararsa yayi kan irin dattakun da ya nuna sakamakon taya shi murna da ya yi kan nasarar kammala wannan rukunin karshe na komawa kasar kan tafarkin dimokiradiya inda ya kara da cewar ''ina kara tabbatar muku da cewa zan rungumi kowa mu tafi tare. Ba abin da ya rage mana bayan gama zabe illa mu fuskanci kyautata gaba."

Kasashen duniya dai musamman ma na yankin gabas ta tsakiya sun taya Tunisiya murnar komawa kan tafarkin dimokradiyya wanda da dama ke cewar boren da suka yi da ya haifar da juyin juya hali ba fadi kasa banza ba.

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani

Bincika karin bayani