1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

NATO: Cigaba da yaki da ta'addanci

September 11, 2021

Sakataren kungiyar tsaro ta NATO Jens Stoltenberg ya ce kawancen kungiyar zai cigaba da yaki da ta'addanci a duniya.

https://p.dw.com/p/40CrR
NATO Secretary General Jens Stoltenberg
Hoto: Francisco Seco/Pool/AP/picture alliance

Jens Stoltenberg ya sha wannan alwashin ne yayin nuna ban girma ga wadanda harin ta'addancin ranar 11 ga watan Satumbar shekarar 2001 ya rutsa da su a cibiyar kasuwancin ta duniya da ke Amirka.

Yayin bikin tunawa da ranar a Hedikwatar kungiyar da ke birnin Brussels fadar gwamnatin kasar Beljium, Stoltenberg ya ce kungiyar zata cigaba da taka rawar da ta ke yi a yaki da ta'addanci.

A yayin bikin an yi kasa-kasa da tutocin kawance 30 don karrama kimanin mutum dubu uku da suka mutu a harin da Al-Qaeda ta kai, hari mafi muni a tarihin Amirka. Amirka da kawancen NATO dai sun mamaye Afganistan bayan harin a wancan lokacin, tare da kwace ikon kasar a hannun kungiyar Taliban da ke da tsattsaurar ra'ayin addinin Islama.