1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Namibiya: 'Yan kasar sun bukaci biyan diyya

May 29, 2021

Wasu 'yan Namibia sun bukaci Jamus ta biya diyya ga iyalan mutanen da aka hallaka a zamanin da ta yi wa kasar mulkin mallaka maimakon tallafin raya kasa da ta yi alkawarin bayarwa.

https://p.dw.com/p/3uAE7
Berlin Proteste gegen Kolonialverbrechen in Namibia
Hoto: Paul Zinken/dpa/picture alliance

Hukumomi a Namibiya sun bayyana farin cikinsu dangane da abin da gwamnatin Jamus ta yi na amince wa da kuskuren da ta yi na kisan kare dangi a kan kabilun Herero da Nama a zamanin mulkin mallaka. 

Jamus dai ta yi mulkin mallaka a yankin da yanzu ya kunshi kasar Namibiya, inda Jamus din ta bayyana kudurinta na bayar da gudunmawar Euro biliyan daya da miliyan dari uku don ayyukan raya kasa a Namibiya a maimakon diyya.

Sai dai wasu 'yan Namibia mazauna Jamus sun bukaci gwamnatin ta Jamus ta biya diyya ga iyalan mutanen da aka hallaka a zamanin mulkin mallaka maimakon gudunmawar raya kasa da za ta bayar.

Batun tallafin dai ya zo ne sakamakon wata zanga-zanga da ta barke a kasashen biyu na Jamus da Namibiyar kan bukatar biyan diyyar wadanda Jamus din ta hallaka da kuma daukar nauyin wasu manyan ayyukan cigaba a kasar da aka yi wa mulkin mallaka a maimakon ban hakuri kawai.