1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nakiya ta hallaka sojoji a Nijar

Abdoulaye Mamane Amadou MNA
August 14, 2019

A Jamhuriyar Nijar sojoji hudu sun hallaka sakamakon taka wani abin fashewa da motarsu ta yi a yankin Diffa da ke fama da hare-haren mayakan Boko Haram.

https://p.dw.com/p/3NrfV
Niger Soldaten
Hoto: Getty Images/AFP/I. Sanogo

Wata majiya daga sojan kasar Nijar ta tabbatar da faruwar hatsarin a tsakanin garuruwan Toumour da Bosso da ke makwaftaka da Najeriya tun a ranar Asabar, to amma sai dai ba a samu cikakken labarin faruwar lamarin ba saboda shagulgulan babbar Sallah.

Sojojin kawancen kasashen Nijar Najeriya, Chadi da Kamaru, na ci gaba da kara matsin lamba a yaki da kungiyar Boko Haram a yankin tabkin Chadi yankin da kungiyar ke samun malaba.

Sojojin hudu na Nijar sun gamu da ajalinsu ne sakamakon taka wani abin fashewa da motarsu ta yi a yankin Diffa da ke fama da hare-haren mayakan Boko Haram.