Nakiya ta hallaka sojoji a Nijar
August 14, 2019Talla
Wata majiya daga sojan kasar Nijar ta tabbatar da faruwar hatsarin a tsakanin garuruwan Toumour da Bosso da ke makwaftaka da Najeriya tun a ranar Asabar, to amma sai dai ba a samu cikakken labarin faruwar lamarin ba saboda shagulgulan babbar Sallah.
Sojojin kawancen kasashen Nijar Najeriya, Chadi da Kamaru, na ci gaba da kara matsin lamba a yaki da kungiyar Boko Haram a yankin tabkin Chadi yankin da kungiyar ke samun malaba.
Sojojin hudu na Nijar sun gamu da ajalinsu ne sakamakon taka wani abin fashewa da motarsu ta yi a yankin Diffa da ke fama da hare-haren mayakan Boko Haram.