1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya za ta fara cinikin zinare

Binta Aliyu Zurmi
July 16, 2020

Mahukunta a Najeriya na fatan dogara kan arzikin karkashin kasa na gwal da Allah ya huwace wa kasar wajen samun dalar Amirka miliyan dari biyar a shekara don samar da aikin yi ga matasa.

https://p.dw.com/p/3fRed
Goldabbau im Amazonas
Hoto: Peter Yeung

A yayin da ya kaddamar da shirin na cinikin zinare a fadar gwamnatin kasar a wannan Alhamis a birnin Abuja, shugaban tarayyar Najeriya Muhammadu Buhari ya ce yana san ran samar da ayyukan yi ga sama da mutum dubu 250 a karkashin wannan shiri.


An kuma kaddamar da shirin ne  tare da cinikin wani danyen zinare daya kai kilo 12.5 da masu hakar zinarin na jihar Kebbi suka kai ga hakowa sannan kuma babban bankin kasar na CBN ya biya dalar Amirka  dubu 800 kansa.

Karkashin wannan shirin shugaba Buhari ya ce za a ba da lasisin hakar danyan gwal din, wanda ya ce babu shi a baya da kuma ake tunanin yana daga cikin hummun habaisin tashin hankula a shiyoyin Arewa maso yammacin kasar.