1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kotu ta amince da sake tsara bayanan na'urar BVAS

Uwais Abubakar Idris ZMA
March 8, 2023

Kotun daukaka kara ta Najeriya ta amince da bukatar da hukumar zabe mai zaman kanta wadda ta nemi da a bata izini ta sake tsara bayanan nau'rar zabe ta BVAS.

https://p.dw.com/p/4OPqd
Na'urar BVAS ta zabe a Najeriya
Na'urar BVAS ta zabe a NajeriyaHoto: BENSON IBEABUCHI/AFP

Wannan hukunci da kotun daukaka karar ta Najeriya ta yanke ya zama raba gardama a kan wannan batu da ake kiki-kaka a kansa, domin da wannan hukumar zabe ta samu uzuri na sake tsara bayanan da ke cikin na'urar ta Bvas domin su dace da zaben gwamnoni da za'a yi a jihohi 30 na Najeriyar.

Alkalan kotun su uku da suka amince da hukuncin karkashin jagorancin mai sharia Joseph Ikeyegha sun ce ba za'a hanawa hukumar zabe wannan ba saboda zaben.

Dan takarar neman shugabancin Najeriyar Peter Obi dai ya kasance a kotu wajen shari'ar da aka yi ta daga lokacin farawa daga karfe 2 na rana har zuwa 4:30 tare da lauyansa Barrister Anechebe wanda ya wakilci Obin.

Wani batu da kotun ta yi hukunci shi ne na izinin da jamiyyar Labour ta nema na bata izinin dubawa da kwafan takardun zaben.

A wata shari'ar daban kotun daukaka karar ta amince da bukatar zababben shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu da ya duba kayayyakin zaben da aka yi na shugaban Najeriya a wajen hukumar zaben kasar.