1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutum 49 sun mutu a sanadiyar ambaliyar ruwa a Najeriya

Ramatu Garba Baba
July 16, 2018

Ambaliyar ruwa ta haddasa asarar rayukan mutane akalla 49 a wasu kauyuka da ke karamar hukumar Jibiya a jahar Katsina a yankin arewacin Najeriya.

https://p.dw.com/p/31Z4K
Katsina Flut Nigeria
Hoto: DW/Y. Ibrahim

Ruwan sama kamar da bakin kwarya daga daren ranar Lahadi ya zuwa Litinin ne ya janyo tunbatsar madatsar ruwan Tiga dam, wanda ya haifar da munmunar ambaliya a kauyukan da ke karamar hukumar ta Jibiya.

Amin Waziri shi ne sakataren hukumar bayar da agajin gaggawa a jahar, ya tabbatar da faruwa lamarin da kuma kokarin da gwamnati ke yi na isar da taimako ga mabukata. Wasu kafafen yada labarai a jahar sun ce gidaje fiye da casa'in ne suka salwanta a sanadiyar iftala'in, baya ga asarar dabbobi sama da dari biyu da sittin. A na ci gaba da neman wasu mutanen da iyalansu ba su ji duriyarsu ba tun faruwar lamarin.