1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Kokarin dinke baraka a tsakanin 'yan kasar

February 28, 2019

Bayan kare gwagwarmaya ta tabbatar da mulkin na shekaru hudu, tarrayar Najeriya na neman hanyar dinke barakar da ke barazanar raba kan al’ummar kasar.

https://p.dw.com/p/3EHGA
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da mataimakinsa Yemi Osinbajo
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da mataimakinsa Yemi OsinbajoHoto: Novo Isioro

Tuni dai shugaban kasar ya fara batun hada kai dama kafa gwamnatin da ke da wakilcin kowa, bayan wani yakin neman zabe mai zafin da kasar ta dauki lokaci tana fuskanta. An dai kai ga karawa tsakanin 'yan boko da talakawa na kasar da tsakanin al’ummar kudancin kasar da arewa dama  tsakanin mabiya manyan addinan kasar guda biyu. To sai dai kuma an kare da gudanar da zaben da ke dada nuna alamun baraka cikin kasar, bayan wata musayar yawu mai zafi a cikin kafafe na zumunta a tsakanin matasan na Kudu da na arewa game da yadda sakamakon ya kasance.