Wani hari da aka kai a Cocin Katolika da ke garin Owo a jihar Ondon Najeriya yayin da ake tsaka da ibada, ya janyo asarar rayukan mutane 50. Maharan sun kai harin ne da abubuwa masu fashewa da kuma bindigogi, inda suka sace Limamin Cocin. Ba kasafai ake samun irin wannan harin ba, a yankin Kudu maso Yammacin Najeriya.