Najeriya: Boko Haram ta halaka sojoji 15
August 10, 2018Talla
Wani jami'in hukumar agajin gaggawa na NEMA da ya nemi a sakaye sunansa, ya bayar da labarin yadda mayakan suka bude wuta da bindigogi kan sojojin da jami'in na su guda a yayin da suke tsakiyar aikin katange wani yanki a garin na Damasak. Harin na ranar Larabar da ta gabata ya kasance hari mafi muni a jihar da ta rasa mutum fiye da dubu talatin a sanadiyar ayyukan ta'addanci.
Mayakan na Boko Haram na ci gaba da kai hare-hare nan da can duk kuwa da kokarin da hukumomin kasar ke yi don ganin an dakile ayyukansu da kuma tabbatar da tsaro a yankin gabanin babban zaben kasar.