1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Bada tallafin ga kudi gwamnatocin jihohi

January 13, 2017

Fiye da kudi Naira miliyan dubu dari biyar da ashirin da biyu ne gwamnatin Tarayyar Najeriya ta bai wa jihohin kasar domin samun zarafin biyan maikatansu albashi da kuma gudanar da ayyukan raya kasa.

https://p.dw.com/p/2VmrC
Nigeria Kabinett Muhammadu Buhari Präsident
Hoto: Reuters/A.Sotunde

Daga cikin adadin kudi Naira miliyan dubu 522 da miliyan 74 da aka samu daga biyan bashin fiye da kima na Paris Club da London tare da wasu cibiyoyin kudi na ketare, an rabar wa jihohin Najeriya 35 ne kudaden baki daya.

Kashim Shettima Gouverneur Bono Nigeria
Gwamnan jihar Borno Kashim ShettimaHoto: DW/U. Shehu

Bincike ya nunar cewar kowace jiha da irin abin da ta samu daga wannan adadin kudi, inda wasu jihohi kamar su Lagos, Bayelsa, Kaduna, Rivers da wasun su saka sami fiye da Naira miliyan dubu 14, wasu jihohi kuwa irin su Benue da Bauchi, sun sami fiye da Naira miliyan dubu 11 yayin da jihohi irin su Filato da Nasarawa kuwa sun sami fiye da Naira miliyan dubu 8 ne daga kudin na Paris Club.

Wasu jihohi irin su Benue da Bauchi, rahotanni sun nunar cewar gwamnatocin jihohin na kokarin ganin sun sauke wannan nauyi na albashi amma jihohi kamar su Eketi bincike ya nuna har yanzu lamarin bai canza zani ba, inda ma'aikatan jihar suka karbi albashin wata guda kachal daga cikin kudi naira miliyan takwas da milyan 877 da aka basu. Don haka Shugaba Buhari cikin jawabin sa na karshen shekara ya yi wa gwamnatocin jihohi gargadi kan wannan kudi.

Nigeria Parlamentspräsident Aminu Tambuwal
Gwamnan jihar Sokoto Aminu TambuwalHoto: picture alliance/Photoshot

Yanzu abin jira a gani shi ne yadda gwamnatocin jihohin kasar za su sarrafa kudaden da aka basu ta hanyar da ta kamata, kasancewar gwamnatin Tarayya ta lashi takobin sa ido wajen ganin ba'a ci gaba da watanda da dukiyoyin jama'a ba kamar yadda aka saba a baya.