1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rudu a 'yancin majalisun jihohin Najeriya

June 9, 2020

A wani abu mai kama da lekowa tare da komawa gidan jiya, an dakatar da amincewa da mai da umarni na 10 na shugaban Najeriya da ya tabbatar da 'yancin kishe kudi na majalisun jihohi da bangaren shari'arsu.

https://p.dw.com/p/3dXxO
Niger Treffen der afrikanischen Union in Niamey - Muhammadu Buhari
Shugaban Najeriya Muhammadu BuhariHoto: Getty Images/AFP/I. Sanogo

Duk da cewar sashi na 121 na kundin tsarin mulkin Tarayyar Najeriya ya tanadi 'yancin cin gashin kai ga majalisun dokoki da bangaren shari'a na jihohin kasar, karfin fada ajin gwamnonin ya hana aiwatar da wannan sashe mai tasiri ga makomar dimukuradiyyar kasar.

Wani yunkuri a bangaren fadar gwamnatin kasar da ta fitar da umarni na yin hakan dai, ya janyo murna cikin Najeriyar da ke fatan 'yancin na iya kai wa ga samar da ingantaccen tsarin dimukuradiyya a daukacin matakai na gwamnatin kasar guda uku.

Nigeria Homosexualität Polizei-Razzia in Lagos
Bangaren shari'a na neman 'yanciHoto: Reuters/T. Adelaja

To sai dai kuma matsin lamba daga gwamnonin kasar na shirin mayar da hannun agogo baya, a Najeriyar da ta dauki lokaci tana neman 'yanci na ragowa na bangarorin mulkin guda biyu na jihohin, amma kuma ba nasarar har ya zuwa yanzu.

An jima ana dako

Tun daga Obasanjo zuwa ga gwamnatin marigayi Umaru 'Yar Adua da ma ta tsohon Shugaba Goodluck Jonathan dai, an dauki lokaci ana fafutukar tabbatar da 'yancin 'yan dokar ba tare da kai wa ya zuwa nasara ba. Kafin sabon umarni na 10 da a karkashinsa shugaban da ke kai yanzu ya ce ko dai gwamnonin su mika wuya ga tabbatar da 'yancin kisan kudin, ko kuma kwamitin rabon kudin kasar ya hana musu nasu.

Nigeria National Assembly
Gwamnoni ba son 'yanci ga majalisunsuHoto: Nigeria Office of the House of Representatives

Wani taro a tsakanin wakilan gwamnonin da shugaban kasar ya kama hanyar mayar da tsarin gidan jiya, tare da bai wa gwamnonin nasarar dakatar da shirin da masu sharhi ke fatan ka iya kai wa ga bude danba ta tabbatar da dimukuradiyya  mai tasiri cikin kasar.

Akwai sauran aiki

Kayode Fayemi dai na zaman shugaban kungiyar gwamnonin kasar, da kuma ya ce da akwai sauran gyara a cikin sabon tsarin na gwamnatin ta Abuja.

Ana dai zargin komawar da dama a cikin majalisun  dokokin da ma alkalai na jihohin ya zuwa 'yan amshin shata maimakon sauya makomar al'umma a jihohinsu, a cikin tsarin da ke bukatar sauyi a ko'ina. Kuma a tunanin Barrister Buhari Yusuf  da ke zaman wani lauya mai sharhi, a batun dokokin kasar ana bukatar jan aiki a bangaren Shugaban Buhari kafin mika wuyan gwamnonin da ke kisa suna shan romo a cikin tsarin na yanzu.