1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya za ta daina ba da tallafi a kan mai

Abdourahamane Hassane
November 25, 2021

Gwamnatin Najeriya ta tsara biyan marasa karfi sama da milyan 30 Naira dubu biyar domin rage masu radadin janye tallafin man fetur da ta ke shirin yi a tsakiyar shekarar 2022.

https://p.dw.com/p/43TH2
Erdöllraffinerie in Nigeria
Hoto: Construction Photography/Photoshot/picture alliance

Wannan al'amari dai na janye tallafin da zai fara aiki a cikin sabuwar shekara 2022 ya janyo martanin al'ummar kasar cikin bacin rai wadanda ke korafin cewar kasar za ta kara shiga wani mawuyacin hali. A bayyane take a fili janye tallafin zai sanya man fetir yin tsada a Najeriyar, inda kamfanin albarkatun main a kasar ya dade da hasashen zai iya kai Naira 400 kowace lita guda, wannan ya sanya gwamnatin tsara bai wa marasa galihu milyan 30 zuwa 40 talafin kudin shiga mota na Naira dubu biyar. Bankin duniya ya dade da nuna cewa tallafin mai ne ke yi wa Najeriya dabaibay, abin da za’a sa a ga jnaye tallafin zai zaburara da tattalin arzikin Najeriya. Daga kasa mun tanadar muku a rahotanni.