1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane uku sun hallaka a Sokoto

March 13, 2013

Musayar wuta tsakanin sojoji da 'yan bindiga ya hallaka mutane uku a jihar Sokoton Najeriya, waɗanda ake zargi 'ya'yan ƙungiyar Boko Haram ne

https://p.dw.com/p/17w81
Nigeria/Kriminalität/Terrorismus Schlagworte: Sokoto, Nigeria, Kidnapper, Geiseln, Terror, Boko Haram Wer hat das Bild gemacht?: Aminu Abdullahi Abubakar (DW Korrespondent) Wann wurde das Bild gemacht?: 09.03.2012 Wo wurde das Bild aufgenommen?: Sokoto / Nigeria Bildbeschreibung: Bei welcher Gelegenheit / in welcher Situation wurde das Bild aufgenommen? Wer oder was ist auf dem Bild zu sehen? Bild 1: Haus in dem Radikalislamisten in Sokoto Nigeria zwei europäsche Geiseln getötet haben.
Hoto: DW/A.Abubakar

Rundunar sojin Najeriya dake sokoto a safiyar yau ta share sao'i bakwai tana musayar wuta, bayan da ta kai wani samame sabbin gidajen gwamnati da ta baiwa ma'aikata na Bado Quaters, inda wasu suke kyautata zaton cewa yan kungiyar Boko Haram ne da suka fito daga Jihar Bauchi.

Rahotanni sun ce an kashe uku daga cikin su an kuma kama wata mata guda da yaran su shidda a lokacin samamen.


Hukumomin sojin sun yi amfani da wani rahoton sirri da suka samu ne suka kai samame tun karfe 4 na safiyar yau Labara. A lokacin samamen an tarar da makamai ƙirar zamani da mutanen ke amfani da su.


Yanzu haka rundunar hadin gwiwa na soji da yan sanda a Sokoto sun samu tarwatsa mutanen sun kuma rusa gidan nasu. Babban comandar sojin Najeriya a Sokoto Muhd Tasiu Ibrahim ya tabbatar da kakkabe barazanar mutanen da kuma wannan mazaunin nasu a Sokoto.

Mawallafi: Aminu Abdullahi Abubakar
Edita: Pinaɗo Abdu Waba