1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane sun mutu a rikicin zaben Indonesiya

Abdul-raheem Hassan
May 23, 2019

'Yan sanda sun ce kura ta lafa a birnin Jakarta bayan kame daruruwan mutane da ake zargi da haddasa rikicin, amma akwai sauran kallo kan matakin dan takara Prabowo Subianto na kalubalantar sakamakon zaben.

https://p.dw.com/p/3IxqR
Indonesien Nach den Anschlägen
Hoto: picture-alliance/AA/A. Raharjo

'Yan sanda sun tabbatar da mutuwar mutane bakwai a Jakarta babban birnin kasar Indonesiya bayan barkewar rikici sakamakon zanga-zangar lumana kan ayyana Shugaba Joko Widodo a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasar.

Wannan dai shi ne karo na biyu da Shugaba Widodo ke kada abokin takararsa Prabowo a takarar shugabancin Indonesiya, amma 'yan adawa na zargin gwamnati ta amfani da ikonta wajen yin magudin zabe.