1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Tattalin arziki

Mutuwa a wajen hakar ma'adanai na Afirka ta Kudu

Binta Aliyu Zurmi
December 8, 2019

Mutane hudu sun mutu lokacin da dutse ya fada musu a inda ake hakar ma'adinai na karkashin kasa a Afirka ta Kudu.

https://p.dw.com/p/3UQPx
Südafrika | Goldmine Sibanye Gold's Masimthembe
Hoto: Reuters/M. Hutchings

A Afrika ta Kudu mutane hudu sun mutu yayin da wani mutum guda ya jikkata bayan da dutse ya fada ya ruife su a  a wajen da suke hakar ma'adinai, kamfanin da ma kungiyar masu hakar ma'adainai.

Kungiyar masu hakar ma'adainai ta kasar Afirka ta Kudu ba ta ji dadin yadda kamfanin da ke aikin a wajen ya gaza ba wajen samar da wata hanyar fita ba a lokacin aukuwar hadari irin wannan. Mai magana da yawun kungiyar ta masu hakar ma'adainai ya ce dutsen ya rufta ne biyo bayan wata girgizar kasa da aka samu a yankin.

Kamfanin na Village Main Reef da ya rasa ma'aikatansa ya ce ba zai ce komai ba har sai an gama fito da mutane da suka mutu an kammala bincike kafin su yi bayani.