1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane fiye da 20 sun mutu a Potiskum

November 3, 2014

Rahotanni daga jihar Yobe a Najeriya na cewa, akalla mutane 23 ne aka tabbatar da cewa sun rigamu gidan gaskiya a harin kunar bakin waken da aka kai a Potiskum.

https://p.dw.com/p/1DgJr
Hoto: AFP/Getty Images

Harin dai an kaishi ne kan Musulmi mabiya mazhabar Shi'a da ke yin zanga-zangar lumana ta muzahara ranar Ashura da suka saba yi duk shekara domin tunawa da kisan gillar da aka yiwa Imam Hussaini jikan Annabi a lokacin yakin Karbala a kasar Iraki. Dan kunar bakin waken dai ya shiga cikin masu muzaharar kafin daga bisani ya tashi bam din da ke jikinsa a tsakiyar su dai-dai wata kasuwa a garin na Potiskum da ke jihar Yobe wadda ke fama da tashe-tashen hankulla na Boko Haram.

A wani labarin kuma a daren wannan Lahadin ne wasu mutane dauke da makamai suka kai hari a wani gidan kaso na birnin Lokoja dake jihar Kogi, inda suka kashe mutum guda tare da fitar da firsinoni a kalla 144. Adams Omale shine jagoran masu tsaron wannan gidan kaso kuma ya tabbatar da faruwar lamarin inda ya ce a halin ynzu an yi nasarar kamo 26 daga cikin firsinonin da suka tsere din.

Mawallafi: Salissou Boukari
Edita : Umaru Aliyu