Mutane fiye da 20 sun mutu a Potiskum
November 3, 2014Harin dai an kaishi ne kan Musulmi mabiya mazhabar Shi'a da ke yin zanga-zangar lumana ta muzahara ranar Ashura da suka saba yi duk shekara domin tunawa da kisan gillar da aka yiwa Imam Hussaini jikan Annabi a lokacin yakin Karbala a kasar Iraki. Dan kunar bakin waken dai ya shiga cikin masu muzaharar kafin daga bisani ya tashi bam din da ke jikinsa a tsakiyar su dai-dai wata kasuwa a garin na Potiskum da ke jihar Yobe wadda ke fama da tashe-tashen hankulla na Boko Haram.
A wani labarin kuma a daren wannan Lahadin ne wasu mutane dauke da makamai suka kai hari a wani gidan kaso na birnin Lokoja dake jihar Kogi, inda suka kashe mutum guda tare da fitar da firsinoni a kalla 144. Adams Omale shine jagoran masu tsaron wannan gidan kaso kuma ya tabbatar da faruwar lamarin inda ya ce a halin ynzu an yi nasarar kamo 26 daga cikin firsinonin da suka tsere din.
Mawallafi: Salissou Boukari
Edita : Umaru Aliyu