1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane 85,000 sun fice daga Falluja

Abdul-raheem HassanJune 24, 2016

Majalisar Dinkin Duniya ta ce mutane sun fice ne daga Falluja saboda yakin da ake yi tsakanin dakarun gamnatin Iraki da na 'yan tawaye.

https://p.dw.com/p/1JCea
Irak Falludscha Zivilisten versuchen die Stadt zu verlassen
Hoto: Reuters/Th. Al-Sudani

Hukumar ba da agajin gaggawa na MDD ta ce sama da mutane dubu tamanin da biyar 85,000 ne suka fice daga birnin Falluja sakamakon yunkurin da dakarun Iraki ke yi na kwato birnin daga hannun mayakan IS. A cikin wannan watan ne dai sojoji kasar suka tsananta kaddamar da sumame a kan mayakan na IS da nufin kwace iko da birnin Fallujan da 'yan IS din suka kafa tunga a ciki.

Hukumar ba da agajin ta ce, ana sa ran wasu kimanin 60,000 za su iso sansanin Khalidya dan samun mafaka. A yanzu dai akalla sama da mutane miliyan uku ne ke gudun hijira a kasar Iraki a tun watan Janairun shekara ta 2014.