1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane 28 sun rasu a zanga-zangar Masar

October 6, 2013

Kimanin mutane 28 ne hukumomin Masar suka ce sun rasu sanadiyyar wani rikici da ya biyo bayan zanga-zangar da magoya baya da masu adawa da shugaba Mursi suka yi.

https://p.dw.com/p/19uW3
Supporters of deposed President Mohamed Mursi and the Muslim Brotherhood clash with anti-Mursi protesters during a march in Shubra street in Cairo October 4, 2013. Clashes broke out in Cairo and several other Egyptian cities on Friday during protest marches staged by supporters of deposed President Mohamed Mursi of the Muslim Brotherhood, security sources and state media said. REUTERS/ Mohamed Abd El Ghany (EGYPT - Tags: POLITICS CIVIL UNREST)
Hoto: Reuters

Rahotanni daga kasar Masar na cewar kimanin mutane 28 ne suka rasu yayin da wasu 94 suka jikkata a wannan Lahadin a wata taho mu gamar da aka yi tsakanin magoya bayan hambararren shugaban kasar Muhammad Mursi da masu adawa da shi.

Gidan talabijin din kasar ya rawaito wani jami'in tsaro na cewar gawarwakin mutanen da suka rasun na da harbin bindiga a jikinsu.

Ya zuwa yanzu dai gwamnatin kasar ba ta ce uffan ba game da wannan balahira da ta auku.

A jiya ne dai gwamnatin ta gargadi al'ummar kasar da su guji yin zanga-zanga da suka dau aniyar yi yayin da a yau ake cika shekaru 40 da samun wata nasara da Masar ta yi a wani yaki da ta yi Izra'ila, gargadin da wasu jama'ar suka yi watsi da shi.

Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Usman Shehu Usman