1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana zaben shugaban kasa

Ramatu Garba Baba
October 15, 2019

Al'ummar kasar za su fita rumfunar zabe don kada kuri'unsu a babban zaben da ke tattare da barazanar tsaro, tuni hukumar zaben kasar ta dakatar da zabe a wasu rumfuna goma saboda matsalar tsaron.

https://p.dw.com/p/3RI8z
Wahlen in Mosambik
Shugaba Felipe Nyusi a lokacin da ya ke kada kuri'arsaHoto: Getty Images/AFP/G. Guercia

Masu sharhi kan lamuran siyasa na ganin cewa duk da farin jinin jam'iyyar adawa ta Renamo, da wuya ta iya kayar da Jam'iyyar mai ci ta Frelimo da ta mulki kasar tun bayan da ta sami 'yanci kai a shekarar alifa da dari tara da saba'in da biyar (1975)  Shugaba Filipe Nyusi dan shekaru sittin da haihuwa na fatan yin tazarce a wa'adi na biyu da zai ba shi damar mulki na wasu shekaru biyar.

Kasar da ke farfadowa daga iftala'in guguwa da ta raba kusan miliyan biyu da muhallinsu na fama da hare-hare 'yan bindiga musanman a yankin Arewacin kasar, wanda ya haifar da tarnaki a kokarin gwamnati na da gudanar da ayyukan raya kasa. Mutum akalla miliyan goma sha uku aka yi wa rejista don kada kuri'a wanannan zaben na yau. Daga karfe bakwai na safe a gogon kasar za a bude rumfunar zaben ana kuma sa ran jin sakamakon zaben a ranar Alhamis mai zuwa.