Moroko: Mutum 15 sun mutu a turmutsitsi
November 19, 2017Talla
Ma'aikatar harkokin wajen kasar ce ta sanar da faruwar lamarin inda ta ce an soma gudanar da bincike don sanin musababin aukuwar yamutsin a wannan yankin kasar da ke fama da tsananin talauci.Wani shedan gani da ido ya ce lamarin ya auku ne a yayin da daruruwan mata da suka hadu a harabar gidan wani attajiri da ya saba rabon kayan abinci ke rige-rigen karbar kayan abincin.