1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Merkel ta soke ziyararta a Aljeriya

Zulaiha Abubakar
February 20, 2017

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta dage ziyarar aiki ta yini biyu zuwa kasar Aljeria da ta shirya fara wa a wanna Litinin din 20 ga watan Fabarairun da muke ciki.

https://p.dw.com/p/2XwP3
Shugabara gwamnatin Jamus Angela Merkel
Shugabara gwamnatin Jamus Angela MerkelHoto: Getty Images/S. Gallup

Rahotanni sun nunar da cewa Merkel ta dage wannan ziyarar ne sakamakon rashin lafiyar shugaban kasar Abdelaziz Bouteflika da aka ce ta yi kamari. Kamfanin dillancin labaran kasar ta Aljeriya APS, ya ruwaito cewa Shugaba Bouteflika na fama da matsalar sarkewar numfashi. Tun da fari dai an shirya cewa shugabar gwamnatin Jamus din Angela Merkel za ta ziyarci Aljeriya tare da ganawa da Firaministan kasar a wannan Litinin din 20 ga watan Fabarairun da muke ciki kana a ranar Talata 21 ga watan na fabarairu ta gana da Shugaba Bouteflika.

Dama dai Shugaba Bouteflika ya sha fama da rashin lafiya a shekara ta 2013. Mai kimanin shekaru 79 a duniya da ke zaman tsohon dan gwagwarmaya ne a lokacin neman 'yanci kan kasar kana ya kwashe tsahon shekaru 15 a kan karagar mulki.