1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Merkel ta goyi bayan tsagaita wuta a Gabas ta Tsakiya

May 18, 2021

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta tattauna ta bidiyo da Sarki Abdullah na Jordan kan tashin hankalin da ake gani a Gabas ta Tsakiya.

https://p.dw.com/p/3tZil
3. Ökumenische Kirchentag 2021
Hoto: oekt.de

Tattaunawarsu ta wannan Talata ta nuna bukatar samun tsagaita wuta, a cewar mai magana da yawun shugabar gwamnatin Jamus.

Wannan na zuwa ne a yayin da a dazu da rana, ma'aikatar lafiyar Falasdinu ta ce wani mutum guda daya ya rasa ransa, wasu kuma sun ji munanan raunuka a artabun da aka yi a tsakanin matasan Falasdinawan da sojojin Izra'ila.

Matasan a sassa daban-daban na Izra'ila da yammacin kogin Jodan sun rinka kona tayoyi tare da yi wa sojojin Baniyahudun ruwan duwatsu, a yayin da su kuma sojojin suka mayar da martani da harba hayakin da ke sanya kwalla.