Muna amfani da "Cookies" domin inganta abubuwan da muke wallafawa a intanet. Za ku iya samun karin bayani a kundin kare bayananmu.
A Najeriya an hada dalibai mata 'yan makarantar sakandaren Jangebe na jihar Zamfara da aka yanto daga hannun mahara ga iyayensu Zuwa sauti
Matakin rufe tashar Mararrabar Jos da mahukunta suka dauka a Kaduna, ya rage cunkoson da ake fama da shi na manyan motocin dakon kaya na tsawon lokaci. Zuwa bidiyo
A cikin shirin za a ji labarai da rahotanni, ciki har da martanin gwamnatin jihar Zamfara bayan umarnin gwamnatin tarayyar na hana jiragen sama yawo tare da hana aikin hakar ma'adinai a jihar, da ake ganin na kara jaza matsalar tsaron. Zuwa sauti
Bayan kazamar zanga-zangar bayan zaben kasa a Nijar, ana ci gaba da tsare daruruwan matasa da aka kama a lokacin boren, abin da masu fafutikar kare hakkin dan Adam ke yin tir da shi.
A cikin shirin za a ji matakin da mahukuntar jihar Katsina da ke Najeriya suka dauka na dakatar da yara mata zuwa makaranta yayin da takwarorinsu maza aka ce su nemi ta jeka ka dawo dake kusa da su.
A cikin shirin na yamma, za a ji rahotanni da labarai a ciki har da yadda wasu 'yan bindiga suka harbe har lahira wasu mata 'yan jarida uku a kasar Afghanistan.
Najeriya ta karbo kashin farko na allurar rigakafin cutar Covid-19 na kamfanin AstraZeneca da aka samar a kasar India. Akwai kuma shirye-shiryen Duniya Mai Yayi da kuma Lafiya Jari.
A cikin shirin bayan labaran duniya za ku ji a Najeriya gwamnatin jihar Zamfara ta yi nasarar kubuto da daliban makarantar sakandaren mata ta Jangebe da aka yi garkuwa da su. Akwai rahoto game da martanin da 'yan Jamhuriyar Nijar ke yi a game da fitar da sakamakon zaben 'yan majalisar dokokin kasar da kotun koli ta yi.
Za a ji Ngozi Okonjo-Iweala ta fara aiki a hukumance a matsayin shugabar kungiyar kasuwanci ta duniya
A cikin shirin za a ji yadda ake kara kulle makarantun boko a arewacin Najeriya.
Kamar sauran wasu jihohin arewacin Najeriya, ita ma gwamnatin Jihar Sakwato ta bayar da umurnin rufe makarantun kawana da ke wajen babban birnin jihar a wani mataki na tunkarar matsalar rashin tsaro.
A cikin shirin bayan labaran duniya akwai rahoto game da halin da iyayen daliban Jangebe da aka yi garkuwa da 'ya'yansu a Zamfarar Najeriya ke ciki, sai rahoto a game da yadda rufe intanet ke kassara kasuwanci a Jamhuriyar Nijar. A Chadi kuma yajin aikin kungiyar kwadago na haifar da komabaya.
Shirin ya kunshi labaran duniya da rahotanni wanda a cikinsa aka ji cewa tsohon sakataren harkokin wajen Amirka Mike Pompeo ya ce wasu 'yan Saudiya da dama na son ganin kasar ta daidaita da Isra'ila.
A cikin shirin za a ji cewa Madugun adawar Nijar da ya ayyana kansa a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasar ya yi kira da agaggauta sakin magoya bayansa, akwai kumwa sharhunan bayan labarai.
An yanke hukuncin daurin gidan yari ga masu rajin girka dimukuradiyyar a yankin Hong Kong na China
A cikin shirin za a ji cewa Amirka ta tabbatar da yariman Saudiyya da kitsa kisan gillar da aka yi wa dan jaridar nan Jamal Khashoggi, akwai kuma shirin Afirka a Mako.
A cikin shirin za a ji shirye shirye irinsu Ku shiga Kulob da Amsoshin Takardunku da shirin wasikun masu sauraro da Ciniki da Masana'antu.
A cikin shirin za a ji Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa duban al'umma da ke gudun hijira a yankunan gabashin Afirka ne ke fuskantar barazanar tsunduma cikin matsananciyar yunwa a wannan shekarar.
Shirin darasin rayuwa ya yi nazari kan yadda annobar corona ta haifar da mummunan illa ga rayuwar ma'aikatan gidajen kallo da yawon bude ido a wasu kasashen nahiyar Afirka.