Muna amfani da "Cookies" domin inganta abubuwan da muke wallafawa a intanet. Za ku iya samun karin bayani a kundin kare bayananmu.
Hukumar samar da tallafin abinci ta MDD za ta dakar da bayar da talafi wa kasar Habasha, Mayakan Al-shebab sun kai hari a wani masaukin baki da ke Mogadishu babban birnin Somaliya. Zuwa sauti
A cikin shirin za a ji a Jamhuriyar Nijar masu sharhi kan harkokin tsaro da ma kungiyoyin fafutuka na kasar ne suka soma tofa albarkacin bakinsu kan batun wani sabon tallafin kudi da kungiyar Tarayyar Turai ta bai wa kasar domin sayen makamai dan ci gaba da yakar kungiyoyin 'yan ta’adda. Zuwa sauti
Shirin ya duba muhawarar da ake ci gaba da yi a Najeriya kan janye tallafin man fetir da ke daukar hankali. Zuwa bidiyo
Shin Wani rin darasi za a iya koya daga irin zamantakewa da cudanya da ake yi da miliyoyin mutane da ake haduwa da su a yayin gudanar da aikin Hajji?
Shirin ya duba tarin matsalolin da mutum zai iya cin karo da su a sakamakon yin aiki ba dare ba rana ba tare da ana hutuwa ba.
Wani sabon labari na cewa China na yunkurin kafa cibiyar lekan asiri a tsibin Kuba da ke kusa da Amirka, Shugaba Macky Sall ya lashi takobin kawo karshen rikicin siyasan Senegal kafin karshen watan Yuni.
Shirin ya kunshi labarai daga sassan duniya da rahotanni da suka hada da halin da ake ciki kan rikicin gwanjon kayayyakin gwamnati a jihar Sokoton Najeriya.
Kammala wa'adin majalisar dokokin Najeriya bayan shekaru hudu tana aikin a yin dokoki da saka ido kan bangaren zartaswa.
Cimma matsaya kan dokokin zaben Libiya inda ake dakon 'yan majalisar dokokin kasar su rattaba hannu kan yarjejeniyar.
Kuna da cibiyar koyar da aikin hannu da ta kai girman wannan a yankinku? Cibiyar Village Artizanal da ke birnin Yamai na Jamhuriyar Nijar na sarrafa abubuwa dabam-dabam ciki har da gyara kayan da aka kawo daga Turai.
A cikin shirin za ku ji cewar Lionel Messi na Ajentina ya yanke shawarar komawa Inter Miami na kasar Amirka da kwallon kafa maimakon Barcelona, inda zai samu kwatankwacin Euro miliyan 200 a kakar wasanni hudu.
A cikin shirin za a ji yadda a Najeriya Kungiyar Dattawan Arewa ke nazarin kamun ludayin mulkin Shugaba Bola Ahmad Tinubu.
Hukumomin Nijar sun nuna wa manoma irin-shukar da ya kamata su yi amfani da su a wannan daminar domin guje wa illar sauyin yanayi.
A cikin shirin za a ji cewa: 'Yan Boko Haram sun yi garkuwa da makiyaya 30 a Arewacin Najeriya, wani dan bindiga dadi ya halaka mutane biyu a bikin yaye dalibai a Amirka.
A Najeriya kungiyar IPOB mai neman kafa kasar Biafra ta janya dokar da ta kakabawa al'ummar yankin kudu maso gabashin Najeriya. A Jamhuriyar Nijar kuwa za ku ji cewa, wata takaddama ta kunno kai tsakanin ministan ilmi mai zurfi da ma'aikatan jami'o'i na kasar.
Gwamnatin kasar Ukraineta ce, harin da Rasha ta kai kasar da ya lalata madatsar ruwanta, laifi ne na yaki.
Sana'ar shayi na ci gaba da samun karbuwa tsakanin matasa a jihar Kano da ke Najeriya. Irin wadannan matasa sun ce sana'ar na taimaka musu wajen samun abun da za su biya bukatunsu na yau da kullum.
Shin ko kuna da masaniya kan wata al'ada da ake yi wa lakabi da "Tarkama"? Shirin Taba Ka Lashe ya yi nazari kan wannan al'ada.
Manyan kungiyoyin kwallon kafa da suka fi suna a wasannin lig-lig a Turai na amfani da kasaitattun wuraren taka leda a biranen Munich da Madrid da London da Milan, lamarin da ya sa suka yi ficce a duniya.