1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mayar da 'yan gudun hijira zuwa Turkiya

Salissou BoukariApril 4, 2016

A wannan Litinin din ce aka soma kwasar 'yan gudun hijira daga tsibirin Lesbos na Girka zuwa Turkiya a wani mataki na soma aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma da Turkiya.

https://p.dw.com/p/1IOr8
Griechenland Flüchtlinge auf Lesbos
Hoto: picture-alliance/AP Photo/P. Giannakouris

Duk kuwa da sukar da kungiyoyin kare hakin dan Adam ke yi wa lamarin, tuni dai da wannan safiya ta Litinin wasu manyan jiragen ruwan kasar Turkiya guda uku suka bar gabar ruwan tsibiran Lesbos da Chios na kasar Girka dauke da 'yan gudun hijirar zuwa kasar ta Turkiya.

Jirgin ruwan na farko dai ya dauki 'yan gudun hijira 131 wadanda akasarinsu 'yan kasashen Pakistan ne da kuma Bangladesh a cewar mai magana da yawun kungiyar Frontex mai kula da sa ido kan iyakokin waje na Tarayyar Turai. Wannan tsari dai ya shafi dukannin 'yan gudun hijirar da suka shiga kasar ta Girka ba bisa ka'ida ba wadanda yawansu ya kai a kalla mutun 6000.