1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Matsayin Jamus kan turawa da sojoji Mali

October 23, 2012

Ministan harkokin wajen Jamus Guido Westerwelle ya ce kasarsa ba za ta bayar da gudunmawar makamai da sojoji domin yakar 'yan ansruddina a arewacin Mali ba.

https://p.dw.com/p/16VLK
President of the African Union-UN peacekeeping panel Romano Prodi (L) and German foreign minister Guido Westerwelle give a press conference at the foreign office in Berlin on October 23, 2012. Prodi, former European Commission chief and Italian Premier, has been named by UN Secretary General Ban Ki-moon as envoy for the Sahel and will coordinate the United Nations' system-wide efforts to finalize and implement the United Nations Integrated Regional Strategy for the Sahel. AFP PHOTO / ODD ANDERSEN (Photo credit should read ODD ANDERSEN/AFP/Getty Images)
Hoto: AFP/Getty Images

Ministan harkokin wajen Jamus ya ce kasarsa a shirye ta ke ta bayar da gudunmawa wajen inganta harkokin tsaro a kasar Mali. Sai dai ya ce ba za ta bayar da gudunmawar makamai ko na sojoji domin fatattakar masu kaifin kishin addinin musulunci daga arewacin kasar ba. Guido Westerwelle ya bayyana haka ne a lokacin da ya gana a birnin Berlin da manzon musamma na Majalisar Dinkin Duniya a kasar Mali Romano Prodi.

Manyan jami'an biyu sun tattauna game da tallafin da Jamus za ta bayar wajen koya wa jami'an tsaron kasar Mali dabarun yaki. D am tun a jiya litinin shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta bayyana hanyoyin da karsata za ta bi wajen taimaka a warware rikicin na Mali.

Kasashe da suke makobtaka da ita Mali ciki har da Mauritaniya da Algeriya na nuna dari dari game da daukan matakan soje akan 'yan Ansaruddine. Yayin da su kuma kasashen yammacin duniya ke nuna fargaba game da rikedewar arewacin Mali zuwa sansanin kulla ayyukan ta'addanci a Afirka. Majalisar Dinkin Duniya na jiran kungiyar ECOWAS ko CEDEAO ta yi mata bayyani dalla dalla game da hanyoyin da za ta bi wajen karbe arewacin Mali daga hannu masu tsananin kishin addinin musulunci.

Mawallafi: Mouhamadou Awal
Edita: Mohammad Nasiru Awal