1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Matakan tsaro gabannin zaben Afghanistan

April 2, 2014

Shugaba Hamid Karzai na Afghanistan na cigaba da daukar matakan tsaro a kasar don tabbatar da cewar ba a samu asarar rayuka ba gabannin zaben da za a yi nan gaba.

https://p.dw.com/p/1BZvl
Afghanischer Präsident Hamid Karzai
Hoto: Johannes Eisele/AFP/Getty Images

Yayin da ya rage kwanaki kalilan kafin gudanar da zaben gama-gari a kasar Afghanistan, hankalin mahukuntan kasar yanzu haka ya karkata wajen girka matakan tsaro domin dakile yunkuri na zub da jini a lokutan zaben.

Tun bayan sanya ranar zaben ne dai aka samu karin tashe-tashen hankula da hare-hare irin na kunar bakin wake musamman ma dai a ofisoshin hukumar zaben kasar da ke sassa daban-daban na kasar, hare-haren da kungiyar nan ta Taliban su ka sha ikirarin aiwatarwa saboda adawar da suka ce su na yi da zaben.

To sai dai duk da wannan matsala da ake fuskanta, 'yan siyasa da dama a kasar na cigaba da yakin neman zabensu, zaben da ake ganin zai kasance cike da rudani duba da yadda jami'an hukumar zaben kasar suka yi korafi cewar 'yan siyasa da jami'an gwamnati na yi wa aikinsu katsalandan.

Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Ummaru Aliyu