1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kara matakan tsaro bayan harin ta'addanci a Faransa

Abdoulaye Mamane Amadou
October 30, 2020

Hukumomi a Faransa sun kara tsarurara matakan tsaro a ko ina cikin fadin kasar biyo bayan wani harin ta'addancin da ya hallaka mutun uku a majami'ar Nice da ke kudancin kasar.

https://p.dw.com/p/3kdHy
Frankreich Nizza | Messerattacke | Präsident Emmanuel Macron
Hoto: Gaillard Eric/abaca/picture alliance

Shugaba Emmaneul Macron ya bayyana kara adadin jami'an tsaron da za su yi sintiri domin tabbatar da tsaro da doka da oda, kana kuma nan gaba a yau a ke sa ran majalisar tsaron kasar zata gudanar da wani zamanta na musaman kan batun,

Kasashe da dama na duniya na ci gaba da nuna alhini da ma yin kakkausar suka kan harin ta'addancin ciki har da na nahiyar Turai da Amirka, inda Shugaba Donald Trump yayi Allah wadarai da abinda ya kira hari kan abukiyar dasawar Amirka wato Faransa.

Su ma dai wasu kasashen Musulmai irin su Turkiya da Saudiya da Iran sun soki harin, a yayin da Tunisya da ake zargin wanda ya kaddamar da harin dan kasar ta ne ta bayya anniyarta na kaddamar da bincike.