Matakan kariyar cutar Ebola a Kwango
July 19, 2019Talla
Babban jami'n wayar da kan al'umma a ma'aikatar lafiya kasar Jamhuriyar Dimukaradiyyar Kwango Dr. Aruna Abedi ya yaba wa gwamnati game da daukar wannan mataki, musamman ganin yadda wasu daga cikin mazauna garin na Goma ke bijirewa wankin hannun da gwajin lafiya. Kasashen da ke makwabaka da Kwango sun shiga fargaba biyo bayan dokar ta bacin da hukumar WHO ta ayyana a Kwango.
Hukumar lafiya ta fara nasarar shawao an cutar Ebola kafin ta sake bullo a gabashin Kwango da wani bangare na Yuganda. Tun a ranar larabane Hukumar Lafiya ta duniya ta ayyana dokar ta baci game da Ebola da nufin daukar kwararan matakan yakar wannan cuta.