1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Masu gwagwarmaya na IS sun ƙwace cibiyoyin tsaro a Kobane

Abdourahamane HassaneOctober 10, 2014

Ƙungiyar ta IS ita ce ke da iko da kusan kishi 40 cikin ɗari na birnin, a dai dai lokacin da Amirka ke ƙara matsa lamba ga Turkiya da ta ba da haɗin kai domin shiga yaƙin.

https://p.dw.com/p/1DTBv
Syrien Kobane IS Terror Grenze Türkei 8. Oktober
Hoto: Reuters/U. Bektas

Rahotanin daga Siriya na cewar 'yan gwagwarmaya masu yin jihadi na Ƙungiyar IS sun ƙwace iko da babbar cibiyar tsaro ta Ƙurdawa da ke a garin Kobane da ke a arewacin Siriyar kan iyaka da Turkiya.

Masu aiko da rahotannin sun ce mayaƙan na IS sun kuma mamaye manyan gine-gine na gwamnatin yankin da wata cibiya ta mayaƙan sa kai na Ƙurdawan.