1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Masar ta tsawaita wa'adin al-Sisi

April 17, 2019

Majalisar dokoki a Masar, ta yi wa kundin tsarin mulkin kasar gyaran fuska, ta yadda zai bai wa Shugaba Abdel Fattah al-Sisi damar ci gaba da mulki har zuwa shekara ta 2030.

https://p.dw.com/p/3GwEv
Ägypten Parlament erstes Treffen
Hoto: picture-alliance/dpa/A.Sayed

Majalisar mai wakilai 596 wadanda galibi ke goyon bayan Shugaba al-Sisi, ta amince da gagarumin rinjaye ne cikin watan Fabrairu kafin ta tabbatar da gyaran a ranar Talata.

Sai dai za a kada kuri'ar ra'ayin 'yan kasa a farkon watan Ramadanan bana, da ke iya kamawa a ranar biyar ga watan gobe na Mayu.

Idan kuma aka kammala kuri'ar ta raba gardama, shugabannin kasa a Masar za su rika yin shekaru shida ne sau biyu.

Hakan kuwa na nufin za a yi wa shugaba mai Abdel Fattah El-Sissi wanda ke wa'adinsa na biyu, karin wasu shekaru biyu na mulkin da yake kai.

Kazalika, zai sake takara a shekara ta 2024.