Hare-haren ta'addanci a Mali na kara ta'azzara
August 9, 2015Talla
Kakakin rundunar sojojin kasar Souleymane Maiga da ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce harin an kai shi ne a kauyen Gaberi da ke arewacin kasar ta Mali. Wannan harin dai na zuwa ne kwana guda bayan da wasu da ake kyautata zaton masu kaifin kishin addini ne suka kai hari a wani Otel ta re da yin garkuwa da mutanen da ke ciki inda suka hallaka mutane 12 ciki kuwa har da jami'an Majalisar Dinkin Duniya hudu kafin a samu nasarar kawo karshen garkuwar da suka yi da mutanen. Kawo yanzu dai babu wani ko wata kungiya da ta dauki alhakin kai harin.