1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Faransa ta hallaka kusa a kungiyar al-Qa'ida

Abdoulaye Mamane Amadou
November 13, 2020

Faransa ta ce ta hallaka wani kusa a kungiyar Al-Qaïda da yayi kaurin suna wajen kaddamar da hare-haren ta'addanci a Mali da kasashen yankin Sahel.

https://p.dw.com/p/3lGLq
Mali Französische Soldaten
Hoto: Daphné Benoit/AFP/Getty Images

Mutumin mai suna Bah Ag Moussa ya gamu da ajalinsa ne a yayin wani farmakin da rundunar tsaron Faransa mai yaki da ta'addanci Barkhane ta kai kan tawagarsa a yankin Menaka da ke Arewa maso gabashin kasar Mali, kana kuma harin ya hallaka wasu mutane hudu da ke yi masa rakiya.

Kakakin ma'aikatar tsaron Faransa ya ce Bah Ag Moussa na daya daga cikin jerin mamanyan hafsansoshin mayakan jihadin, kana kuma yana daya daga cikin masu daukar wa kungiyar GSIM mai alaka da Al-Qaïda mayaka, sannan kuma yana da hannu wajen kitsa kai muggan hare-haren ta 'addanci kan sojojin Mali da da kawayenta.