1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Norway za ta sasanta rikicin Venezuela

Abdul-raheem Hassan
July 8, 2019

Wakilan gwamnatin Venezuela da bangaren adawa za su gana a tsibirin Barbados domin fara tattauna batun kawo karshen rikicin siyasar kasar da ya ki ci yaki cinyewa.

https://p.dw.com/p/3LjMi
Bildkombo Venezuela Guaido Maduro

Kasar Venezuela ta jima tana fama da rikicin shugabancin tun bayan da jagoran adawa Juan Guaido ya ayyana kansa a matsayin shugaban kasa a farkon shekarar 2019, matakin da Shugaba Maduro ke ganin rashin mutunta tsarin dimukuradiyya ne.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce akalla mutane 66 ne suka mutu a kasar sakamakon zanga-zanga a watannin biyar na farkon shekarar 2019, yayin da wani sabon rahoto ya bankado yadda jami'an tsaron gwamnati suka kashe mutane sama da 6,000 da gangan.