1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Macron na son Ursula ta shugabanci EU

Abdoulaye Mamane Amadou
July 2, 2019

Faransa na son a zabi ministar harkokin wajen Jamus daya daga cikin 'yan takarar shugabancin kungiyar tarayyar Turai a matsayin shugaba.

https://p.dw.com/p/3LT2I
Bundestag Ursula von der Leyen
Hoto: picture alliance/dpa/M. Skolimowska

Shugaba Emmaneul Macron na Faransa ya shigar da bukatarsa ta nadin Ursula von der Leyen ministar tsaron Jamus a matsayin sabuwar shugabar hukumar Tarayyar Turai.

Emmaneul Macron ya shigar da bukatar ne ga Angela Merkel shugabar gwamnatin Jamus a yayin ci gaba da taron da kungiyar tarayyar Turai ke gudanarwa yanzu haka a kasar Beljiyam, biyo byan dage ci gaba da taron a jiya saboda rashin samun matsaya.

Jaridar Die Welt ta kasar jamus da ke fitowa kowace rana, ta ambato cewa hatta Donald Tusk shugaban hukumar mai barin gado ya bayar da shawarwarin nada Ursula a matsayin shugabar hukumar.