1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mace-mace a harin bam a Bagadaza

Ahmed SalisuOctober 27, 2014

Mutane akalla 15 ne aka tabbatar da cewa sun rasa rayukansu a harin bam da ya auku a Bagadaza babban birnin Iraki, a cewar jami'an 'yan sanda da na kiwon lafiya.

https://p.dw.com/p/1DcxG
Hoto: Reuters/Stringer

Jami'an 'yan sanda a Iraki sun ce wani harin kunar bakin wake da aka kai a Bagadaza ya yi sanadin rasuwar mutane kimanin goma sha biyar baya ga wasu da dama da suka samu raunuka, wasunsu munana.

Shaidun gani da ido suka ce harin da ya auku dazu kuma an kaishi ne a lardin nan na Karrada da ke da yawan shaguna da gidajen cin abinci inda mabiya tafarkin Shi'a da 'yan Sunni kan gudanar da harkokinsu.

Ya zuwa yanzu dai babu labarin wata kungiya da ta dau alhakin kai wannan harin. Sai dai dama Irakin na fama da hare-hare makamatan wannan, baya ga barazana da take fuskanta daga 'yan kungiyar nan ta IS da ke rajin girka daular Musulunci a Irakin da Siriya.