1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Libiya: Taron majalisar ministoci cikin rudani

Abdoulaye Mamane Amadou MAB
April 21, 2022

Watanni bayan da majalisar dokokin Sebha ta kaddamar da ita, sabuwar gwamnatin Libiya karkashin jagorancin Fathi Bachagha ta yi taron farko na majalisar ministoci.

https://p.dw.com/p/4AG7u
Libyen | Fathi Bashagha kandidiert als Präsident
Hoto: Hazem Turkia/AA/picture alliance

Shugaba Fathi Bachagha da kansa ne ya jagoranci taron, wanda ya kira a sahihance bayan da suka samu tabarrukin majlisar dokokin gabashin kasar, mai tazarar kilo mita 750 da birnin Tripoli.

Ita dai Libiya ta fada rudanin jagoranci ne tun bayan da hamshakin attajiri Abdelhamid Dbeibah da ke jan ragamar mulki a birnin Tripoli tun a shekarar 2020 ya yi kwance da mukaminsa, bayan da majalisar dokoki mai mazauni a birnin Sebha ta nada Bachagha a matsayin sabon firaminista.

Duk da cewa ba shi da wani karfin fada a ji da bangaren zartarwa a birnin Tripoli, firaminista Fathi Bachagha ya ce zai ci gaba da tafiyar da harkokin mulki kamar yadda majalisar ta bukata.