1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Lawyoyi a Niger sun fara wani yajin aiki

Kamaluddeen SaniJanuary 11, 2016

A yau Litinin ne lawyoyi a Jamhuriyar Nijar suka shiga wani yajin aiki biyo bayan zaman majalisar lawyoyin ta kasa da ta yi don nuna fushunta ga gwamnati.

https://p.dw.com/p/1HbL7
Revisionsgericht in Niger
Hoto: DW/M. Kanta

Majalisar lawyoyin ta dauki wannan matakin ne don nuna bakin cikin kan kame-kamen da ake yi ma wasu 'yan siyasar adawar kasar da ake tuhumar da hannu a yunkurin kifar da mulkin da bai ci nasara ba.

Shugaban majalisar lawyoyin Samna Soumana Daouda ya ce ya na da kyau a gurfanar da wadanda ake zargi a gaban kotu ba wai a ci gaba da tsaresu ba.

Yanzu haka dai al'amura na ci gaba da zafafa a yayin da ake tsare da Hama Amadou dan takarar shugabancin kasar da katun kundun tsarin mulki ta amince da takararsa.