1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Larabawa sun gaza tallafawa Palasdinu da kudi

February 21, 2006
https://p.dw.com/p/Bu7h

Mideast

Ministocin harkokin waje na kasashen larabawa sun gaza cimma yarjejeniya a dangane da bawa Palasdinu tallafi ,akarkashin gwamnatin Hamasa dangane da sabanin raayi kann tallafi daga kowace kasa.Kasashe uku daga cikin kungiyar ne suka bada tallafin kudi wa palasdinawan,inji jamian Algeria a taron wakilan kungiyar daya gudana zuwa tsakar daren jiya a birnin Algiers.

Sakataren kungiyar kasashen larabawa Amr Moussa da ministan harkokin wajen Algeria Abdelaziz Belkhadem sun kaddamar da asusun neman tallafi daga kasasgen ,domin agazawa sabuwar gwamnatin Palasdinu.To sai dai a taron da suka gudanar da manema labarai,jamian sunki bayyana kasashen da suka bayyana adfawa da wannan yunkuri.Amr Moussa yace dakatar da tallafi da kasar Amurka da Kungiyar gamayyar Turai sukayi barazana,zai haifarwa palasdinawan matsaloli.A dangane da hakane ya jaddadawa kasashen larabawan cewa,wannan tallafin zasu bayar ne wa jamaar palasdinu ,amma bawa Hamas ba.