1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kwango: 'Yan adawa na shakku da shirin zabe

Abdul-raheem Hassan MNA
October 31, 2018

Babbar jam'iyyar adawa a jamhuriyar dimukuradiyyar Kwango ta Union for Democratic and Social Progress, ta ce ba a shirya yin zabe ba kuma 'yan adawa ba su gamsu da matakan tsaro ba.

https://p.dw.com/p/37PuC
DR Kongo Wahlkampf in Kinshasa
Magoya bayan 'yan adawa lokacin wata zanga-zanga a gaban kotun kolin kasa da ke birnin KinshasaHoto: Getty Images/AFP/S. Tounsi

Wannan dai na zuwa ne kwana guda bayan da rundunar tsaron kasar ta ba wa hukumar zaben kasar tankunan yaki 150 da jiragen yaki da dama a wani mataki na inganta tsaro a lokutan gudanar da zaben.

Duk da haka dai babbar jam'iyyar adawa a jamhuriyar dimukuradiyyar Kwango wato Union for Democratic and Social Progress UDPS, ta ce ba a shirya yin zabe ba kuma 'yan adawa ba su gamsu da matakan tsaro ba.

Wani zaben jin ra'ayin jama'a ya nuna cewa duk da irin rikita-rikitar da ake fama kan zaben, amma 'yan takara biyu daga jam'iyyun adawa na kan gaba a takarar shugabancin kasar.