1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An yi sulhu a tsakanin Ruwanda da Kwango

July 6, 2022

Kasashen biyu dai sun rika jifan juna da bakaken maganganu, har ma daga baya lamarin ya kai ga amfani da makami a kan zargin juna da daukar nauyin 'yan tawayen da ke gabashin Kwango mai fama da fitintinu.

https://p.dw.com/p/4Dm6s
Kombibild Felix Tshisekedi und Paul Kagame

Shugabannin kasashen Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango da Ruwanda sun amince sun kawo karshen zaman doya da manjar da suka kwashe makonni suna yi. Fadar mulkin Kwango da ke birnin Kinshasa a cikin wata sanarwa da ta fitar ta ce an cimma wannan matsaya ce a wannan Laraba. 

Sanarwar sasancin Kwango-Kinshasa da Ruwandan dai ta ce kasashen sun tsara yadda za a kawo karshen ayyukan 'yan tawayen M23 da ke halaka musu jami'an tsaro da fararen hula.