Kudurin neman amincewa da kasar Falasdinu
November 29, 2014Talla
Kasar Jordan wadda ta kasance mamba a kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya daga yankin Larabawa za ta gabatar da wani daftarin kudurin da zai sanya wa'adin tsawon lokacin da za a dauka domin girka kasar Falsadinu, a nan da 'yan kawanaki masu zuwa. Shugaban Kungiyar Hadin-kan Larabawa Nabil Araby ne ya tabbatar da wani labari.
A cewar kamfanin dillancin labaran Reuters Babban jami'in kungiyar larabawan ya ce an dade ana kunbiya-kunbiya kan wannan bukata ta samar da kasar Falasdinu, amma abin da ya kasance sabo a wannan karon shi ne Falasdinu da kanta, ta yanke shawarar zuwa Kwamitin Sulhun Majalisar Dinkin Duniya, da daftarin kudurin Larabawa ta hanyar kasar Jordan.