1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Kotu ta saki 'yan farar hula a Nijar

September 29, 2020

Wata kotu a birnin Yamai na Jamhuriyar Nijar ta sallami 'yan fararen hular nan da gwamnatin kasar ke tsare da su kusan watanni shida. 

https://p.dw.com/p/3jAaw
Demokratische Republik Kongo Kinshasa | Nigerianischer Präsidenten Mahamadou Issoufou
Hoto: Presidence RDC/G. Kusema

Rahotanni sun ce a wannan Talata kotun ta saki Maikoul Zodi shugaban kungiyar fararar hula ta "Tournon la page" da Halidou Mounkaila da Moudi Moussa biyo bayan tuhumarsu da yunkurin tada zaune tsaye ta hanyar shirya zanga-zanagar da hukumomi suka haramta.

Ali Idriss daya daga cikin fitattun 'yan fafutuka na Jamhuriyar ta Nijar ya shaida wa wakilinmu na Yamai Mamman Kanta cewa kotu ta saki 'yan farar hular bisa hujjojin da lauyoyi suka gabatar mata.