Kotu ta fara sauraron Muhammad Mursi
July 14, 2013Talla
Ana tsare da mutanen ne a lokacin da aka yi juyin juya halin da ya yi sanadiyyar faɗuwar gwamnatin tsohon shugaban ƙasar Hosny Mubarak,kafin daga bisani a gano cewar sun arce daga gidan tsaron.
Masu yin binciken na buƙatar samun bayyanai kan cewar ko tsohon shugaban da 'yan ƙungiyarsa sun sami tallafin ƙungiyar Hezbullah ta Lebanan ko Hamas ta Falasɗinu a lokacin da lamarin ya faru. Kuma a cikin watan Yuni da ya gabata wata kotun ta ce ƙungiyoyin na Hamas da Hezbullah suna da hannu waja a cikin lamarin.
Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Zainab Mohammed Abubakar