1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Koriya ta arewa tace a shiye take ta bar shirinta na nukiliya

October 10, 2006
https://p.dw.com/p/BugQ

Wani jamiin Koriya ta arewa yace gwamnatin Pyongyang a shirye take ta koma teburin tattaunawa na kasa da kasa akan makamanta,tare kuma da barin shirinta na kera makamin atom muddin dai Amurka ta dauki matakai da suka dace.

Kanfanin dillancin labaari na Koriyan Yonhap ya ruwaito ta bakin jamiin cewa,wannan gwaji yana nufin baiyana aniyarsu ce ta neman zaunawa kan teburin shawarwari da kasar Amurkan.