1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAsiya

Koriya ta Arewa ta harba makami mai linzami a karo na tara

March 5, 2022

Matakin na zuwa ne kwanaki hudu kafin zaben shugaban kasa a Koriya ta Kudu, kuma wannan ne karo na tara a cikin shekarar nan da Koriya ta Arewan ke gwajin makamai masu linzami a tsaka da yakin Rasha da Ukraine.

https://p.dw.com/p/483EJ
Nordkorea Raketentest
Hoto: picture-alliance/AP Images/KCNA

Koriya ta Arewa ta harba makami mai linzamin da ba a kai ga tantance irinsa ba a ta fuskar gabashin tekun Koriya. Jami'an makwabciya Koriya ta Kudu da kasar Japan ne suka sanar da haka a wannan Asabar.

 

Duk da dandana tankunkuman karya tattalin arziki da kasashen duniya suka kakaba mata a kan mallakar makaman nukiliya, Koriya ta Arewa ta yi fatali da tayin Amurka na tattaunawa.

 

A shekara ta 2019, an rabu dutse a hannun riga a tattaunawar Shugaba Kim Jong-un da tsohon shugaban Amirka Donald Trump a game da makaman nukiliyar Koriya ta Arewa.