Najeriya: Buhari ya gana da shugabannin addinai
March 29, 2019An dai kai ga tayar da jijiyar wuya cikin fagen siyasar tarrayar Najeriya sannan kuma kawunan sun kai ga rabewa a bisa turbar addini a fagen siyasar. An ma kai ga zabukan kasar a cikin imanin rawa ta malaman addinin da suka fito fili da nufin nuna gwanayensu a zabukan kasar mai tasiri. To sai dai kuma ana shirin sake hade kai yanzu tare da wani taro na shugaban kasar da malaman addinanta biyu da nufin kau da banbancin dama fatan dorawa cikin ginin kasa.
Najeriyar dai ta dauki lokaci tana fuskantar tsomin baki na masu siyasar da ake tallakawa da sakamakon da ke nuna shugaban kasar na tasiri a cikin sashen arewacin kasar a yayin kuma da aboki na hammayarsa ya taka rawar gani a bangaren kudu. To sai dai kuma daga dukkan alamu mahukunta na kasar na neman kaucewa rabuwar addinin tare da wata ganawa a tsakanin shugaban kasar da shugabannin manyan addinan kasar biyu.
Malaman addinin dai na dan jan aikin banbace zamowa fitila ta haska al'ummar da suke yi wa jagora da kuma fakewa a cikin sunan addinin da nufin tunzura magoya baya.