1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kiraye-kirayen kwantar da hankali a Nijar

Mouhamadou Awal BalarabeJanuary 17, 2015

Wasu malaman Islama na Nijar sun yi amfani da kafofin sadarwa wajen yi kira ga masu zanga-zangar da su daina kone-kone saboda ya saba wa koyarwar addininsu.

https://p.dw.com/p/1EMBL
Hoto: STR/AFP/Getty Images

Shugabannin addini na Jamhuriyar Nijar sun yi kira ga 'yan kasar da su kawo karshen fashe-fashe da kone-konen da suke yi a wasu biranen kasar, bayan hoton Annabi Muhammad SAW da jaridar barkwanci ta kasar Faransa wato Charlie Hebdo ta sake wallafawa a ranar Laraba da ta gabata. Sama da limamai da kuma wasu Ulama 20 ne suka yi amfani da kafar talabijin a birnin Yamai wajen bayyana wa masu zanga-zanga cewar Islama ba ta amince da rusa wuraren ibada na mabiya addinin Kirista kamar yadda suke yi ba.

Wannan jan kunnen ya biyo bayan da jami'an 'yan sanda a Yamai babban birnin kasar Nijar suka yi amfani da borkono mai sa hawaye wajen tarwatsa taruruwa da aka yi a harabar babban masallaci Jumma'a da niyar gudanar jerin gwano. Lamarin da ya haddasa tashin hankali da kone-konen tayoyi inda aka kona motocin 'yan sanda guda biyu, tare da kona Coci-Coci da dama.

A birnin Maradi ma dai wasu matasa sun kona tayoyi a wasu unguwanni. sai dai jami'an tsaro da ke sintiri cikin birnin sun tarwatsa su. Tuni dai Jakadan kasar Faransa a Jamhuriyar Nijar ya yi kira ga 'yan asalin kasarsa da su yi taka tsan-tsan.