1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kenya za ta janye daga kotun ICC

September 5, 2013

Majalisar dokokin ƙasar ta amince da wani ƙudiri wanda zai buƙaci gwamnatin da ta ɗau matakai domin ficewa daga kotun da ke hukunta manya laifukan yaƙi ta duniya.

https://p.dw.com/p/19cnf
A photo taken on September 5,2013 shows the parliament buildings in Nairobi as deputies were discussing pulling out of the International Criminal Court (ICC). Kenyan lawmakers on September 5 began debating whether the country should pull out of the ICC, in an angry snub to The Hague-based tribunal ahead of next week's trial of Vice President William Ruto. Ruto on September 10 will be in The Hague to face three counts of crimes against humanity for allegedly organizing 2007-2008 post-election unrest that killed at least 1,100 people and displaced more than 600,000. His trial comes about two months ahead of that of President Uhuru Kenyatta, who faces five charges of crimes against humanity, including murder, rape, persecution and deportation. AFP PHOTO / SIMON MAINA (Photo credit should read SIMON MAINA/AFP/Getty Images)
Hoto: Simon Maina/AFP/Getty Images

Tun da farko a yau a ƙasar Hollande da ta ke yin magana Babbar alƙalin kotun Fatou Bensuda ta ce kotun ta ICC za ta ci gaba da shirin gurfanar da shugabanin ƙasar wato shugaban ƙasar Nhuru Kenyatta da mataimakinsa William Ruto.

Dangane da zargin samun su da hanu a cikin tashin hankali da ya biyo bayan zaɓuɓɓukan shekarun 2007, wanda a ciki mutane dubu daya da ɗari biyu suka rasa rayukansu. An dai shirya yin shari'a ta Ruto a cikin watan Satumba kafin a yi ta Nhuru Kenyatta a ranar 12 ga watan Nuwamba da ke tafe.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Umaru Aliyu